Powered By Blogger

Wednesday, December 7, 2011

Ashekarar 2010 zuwa 2011 mun sake fitarr da finafinai karkashin sabon kamfaninmu na shirya finafinai mai suna A.D.S Concept. Ga sunayen su kamat haka:
MADUBI, KYAWUN GANI, SO YACI GARI, ANGO MIJIN AMARYA, BAN AMINCE BA, amma shi yana kan hanya. Dan haka ga masu sha'awar kallon fim na hausa sa iya neman su a kasuwa.

Sunday, March 9, 2008

Monday, August 20, 2007

SADUWA DA MU

Nura Na'iya Gwammaja NNG (Nura Boudah)
1320,Late A.Mohd Bakori Ave,Behind Leader Textile Gwammaja Qtrs,
P.O.Box 13951,Kano Nigeria Cel: 00234(0)8023666093 Stc:00234 (0)7028002399
Priv.e-mail nngkano@yahoo. com

http/www.nuraboudah.blogspot.com

Saturday, August 18, 2007

Friday, August 17, 2007

FIM DIN HAUSA DA NA YI

A shekarar 1997 ne muka gabatar aikin yin wani fim din hausa mai suna "SUMA 'YA'YA NE",a karkashin wata kungiyar gabatar da wasannin kwaikwayo a dabe mai suna Tauraruwa Drama, dake yin taronta a dandalin matasa da ke Fagge,watau (fagge social welfare).
Wannan fim mai suna a sama wanda ya dauki nauyinsa shine Zurkifili Mohd,kuma shine yaron cikin fim din,ya fito ne kuma da wata yarinya wadda daliba ce gare shi,alokacin yana koyarwa a makarantar yan mata dake Gwammaja watau (GGC DALA)wanda daga baya ya dinga fitowa cikin finafinai,daga cikinsu akwai "AISHA","BA'ASI"d.s
To nidai a wannan fim din an dauke nine cikin crew,watau ma'aikatan da suka shirya shi,a matsayin mai daukar hoto (CAMERAMAN)
Bayan wannan fim da na ambata muku a sama,a dai cikin wannan shekara,mun shirya fim mai suna "MUGUN NUFI"na wasu yan dirama ne suma dake a can kwarin gogau.Bayan haka,sai "KOWA YA SAMI RANA"na wani kamfanin shirin fim mai zaman kansa a unguwar Gwammaja. Na kuma yi aiki da kungiyar dabo fim association ita dake a Gwammaja,duk a matsayin Cameraman.
To,daga bisani sai na fara fitowa ta musan cikin finafinai watau (special appearance) na fito a finafinai kamar su,TAWILI (matsayin Sarkin dogarai) sai JAHEED 2 (a matsayin dan tawagar abokin actor Sanin Danja) da dai sauran finafinan da harma yanzu basu fito ba,kuma bazan iya kawo sunayensu ba.
Bayan duk finafinan da na labarta muku a sama,a shekarar 2003 ne kuma na ja ragamar shirya wani fim wanda nine na fito a matsayin jarumi a ciki,kuma nine producer nasa,wannan fim shine "ALIYU"na fito da wannan suna Aliyu kuma yarinyar fim din itace Hadiza Kabara,ta fito da suna Aisha.Wannan fim din ya samu yabo da kuma karbuwa,wanda harma wata mazauniyar Abuja mai suna Amina Abdulmalik,wadda kuma marubuciya ce sosai tayi wa wannan fim sharhi,kuma ta turo shi majalisar fim ta intanet din nan.Domin jin dadin mai karatu ne ma ya sa na dan gutsuro muku wannan sharhi da wannan marubuciya ta yiwa fim din a waccan lokacin,gashi kamar haka:

From: Amina Abdulmalik SHARHIN ALIYU
SUNAN KAMFANI : BOUDAH FILMS PRODUCTION
SUNAN FIM : ALIYU
LABARI : AMINU GARBA DALE
TACE LABARI : MANNIRU MUSA DANTASHA
KWALLIYA :SULAIMAN GAMBO ALAKA
KULA DA KAYA : NURA IBRAHIM BEBI
KULA DA DANDALI:ALIYU FARUK LULUHABIBU ABDULKADIR KABO
JIN DAD’IN Y’AN WASA : BASHIR BIGGY SMALL
K’IRK’IRAR WAK’OK’I : AHMAD MAHMOOD MANNIRU MUSA DANTASHA
RERAWA: AHMAD MAHMOOD,YAKUBU MUHAMMAD,JAMILA SADIQ,HAJARA MOHAMMED,
KULA DA FITILU: ALHAJI ALI IBRAHIM,HAJI ABDUL
HOTON KATI : BOUDAH PHOTOS K/ MAZUGAL
HAD’A HOTUNA: AHMAD LABARAN DANEJI,SULAIMAN A. YAHAYA
D’AUKAR HOTO:SANI MAMBOSASA,AMINU GEMU
KULA DA SHIRYE SHIRYE: ABUBAKAR BABU
SHUGABAN SHIRI: IBRAHIM Y. SINANA
D’AUKAR NAUYI: ALHAJI NURA NA’IYA ,BASHIR NA’IYA
Y’AN WASA: KABIRU MAIKABA; HADIZA KABARA; SHU’AIBULAWAL (KUMURCI); AMINA GARBA; LUBABATU BELLO; HAJIYAZAINAB; HABIBA ABUBAKAR; NURA BOUDAH; ALASAN KWALLI;MANNIRU MUSA; ETC
WAK’OK’I: 4
BA DA UMARNI: SHU’AIBU LAWAL (KUMURCI)
HAJIYA TALATU (LUBABATU BELLO) TA KAI KUKAN MIJINK’AWAR TA ZUWA GA ABOKIN MU’AMALAR TA MAI SUNANAKONGO, DOMIN WAI A CEWAR TA K’AWAR BA TA JIN DAD’INMIJIN , MUSAMMAN TA FANNIN KUD’I. SUKA SHIRYA YADDA ZASU YI DABARA SU CI GALABA AKAN MIJIN K’AWAR.HAJIA ZUHRA (HAJIYA ZAINAB) MATAR ALHAJI (KABIRU MAIKABA) TANA ZAUNE A FALO, SAI TA KIRA ALIYU TA NEMI YAFAD’A MATA DALILIN ZAMANSA A GIDAN.ALIYU YA CE SHI DA YA YI ZATON TA SANI, AMMA TUN DA BATA SANI BA ZAI FAD’A MATA. YA FAD’A MATA CEWA,BAYAN YA YI SHEKARA ASHIRIN WURIN MALAMINSA NA ALLO,SAI WATA RANA MALAMIN YASA SHI A GABA DOMIN YA KAISHI WURIN IYAYEN SA, AMMA SUNA ISA WANI DAJI, SAI Y’ANDABA SUKA TARE SU, BAYAN SUN WAHALAR DASU, SAI KUMA SUKA JEFAR DA SHI AKAN TITI MAGASHIYYAN.ALHAJI DA YARON SA MISBAHU SUKA TSINCE SHI SUKAKAI ASIBITI. BAYAN YA WARKE NE ALHAJI YA KAWO SHIGIDANSA YA RIK’E SHI KAMAR D’A. ALIYU YA GAMA FAD’A WAHAJIYA LABARIN SA, SAI ITA KUMA TA NUNA ALAMAR SON SA.ALIYU YA K’I YARDA, DOMIN YANA JIN BA ZAI IYA CINAMANARUBANGIDANSA BA, YA NEMI TSARI GA ALLAH YA FITA DAGAGIDAN.ALHAJI YANA ZAUNE A FALO SAI ALIYU YA SHIGA YA FARA BASHI SHAWARA DA YASA AKAI AISHA TA DUBO KAKANNIN TA NAWAJEN MAHAIFIYAR TA, DOMIN YA GA TUN DA MAHAIFIYAR TATA RASU BA A KAI TA TA GAISHE SU BA. ANA CIKIN HAKASAIHAJIYA DA KE CAN TANA SAURARE TA SHIGA FALON TA NUNARASHIN AMINCEWAR TA GA WANNAN SHAWARA TA ALIYU.MAGANA DAI HAR TA YI ZAFI TA FARA KUKA. WANNAN YATAYAR DA HANKALIN ALHAJI YA K’I AMINCEWA DA AIKAWA DAAISHA, YA BA HAJIYA HAK’URI YA KUMA BA ALIYU HAK’URI.ALIYU YA FITA DAGA FALO, ITA KUMA HAJIYA TA ZAUNA TAREDAMAIGIDAN TA SUKA FARA RAHA. BA DA DAD’EWA BA ALHAJI YASAKE FITA.AISHA TA YI WANI MAFARKIN SOYAYYA A TSAKANIN TA DAALIYU, DON HAKA TA JE TA SAME SHI A WAJE YANA SHARA TANEMI DA YA FASSARA MATA MA’ANAR MAFARKIN. A NAN NESUKA SHA RAWA DA WAK’A A MAFARKI. BAYAN TA GAMABAYANINMAFARKIN TA, SAI ALIYU YA RAINA KAN SA, DOMIN YANAGANIN AISHA TA FI K’ARFINSA.SUNA CIKIN TATTAUNAWA, SAI KWATSAM HAJIYA TA JE TASAME SU TA FARA ZAGIN ALIYU. ALHAJI DA YARONSAMISBAHU SUKA SHIGA SUKA SAME SU. ALHAJI BAI JI DAD’INYADDA YA SAMI MATARSA TANA D’AGA MURYA AKAN ALIYU BA.HAJIYA TA SHAIDA WA ALHAJI DALILIN D’AGA MURYAR TA WAITA SAMI ALIYU DA AISHA SUNA MAKUSANCIYAR SOYAYYA NE.RAN ALHAJI YA B’ACI MATUK’A YA FARA ZARGIN ALIYU AKANCIN AMANA. AISHA TA YI K’OK’ARI TA FAHIMTAR DAMAHAIFINTA CEWA BA HAKA ZANCEN YAKE BA, AMMA HAJIYA TA TSARETANA TA K’ARA ZUGAWA. DA MISBAHU YA GA ABIN YA CITURA,GA SHI KUMA ALHAJI ZAI JE YA SHIGA JIRGI YA YI TAFIYAKADA YA MAKARA, SAI YA ROK’I ALHAJI CEWA YA BAR KOMAIAHANNUNSA IDAN YA DAWO DAGA KAI SHI TASHAR JIRGI ZAIBINCIKA KOMAI. ALHAJI YA AMINCE HAR MA YA K’ARA MASADADUKKAN NAUYIN KULA DA SHA’ANIN GIDAN KAF. HAJIYA BA TAJI DAD’IN WANNAN ABU BA, HAR DAI TA YI ALLAH YA ISA.ALHAJI DA MISBAHU SUKA TAFI TASHAR JIRGI. AISHA TA CIGABA DA BA ALIYU HAK’URI.ALHAJI YA YI TAFIYA ZUWA HONG KONG TSAWON WATA. HAJIYADA MANGA SUKA YI TA SHEK’E AYARSU. MANGASHI NE MUTUMIN DA HAJIYA TALATU DA NAKONGO SUKA AIKAZUWA GIDAN ALHAJI A MATSAYIN D’AN YAR HAJIA ZUHRA.RANAR DA ALHAJI ZAI DAWO, SAI HAJIYA TA SHAIDA WAMANGA CEWA TA SAMI JUNA BIYU GA SHI KUMA ALHAJI BA YANAN.HANKALIN MANGA YA TASHI, YA SHIGA CIKIN D’AKI YA HAD’AKAYANSA ZAI GUDU. HAJIYA TA BI SHI TANA TA BA SHIHAK’URI,SAI YA CI KARO DA WANI MUTUM A BAKIN K’OFA. MUTUMIN YANEMI HAJIYA DA TA BA SHI MILIYAN D’AYA. HAJIYA BA TAJIDAD’IN ZUWAN MUTUMIN BA BA TARE DA YA SANAR DA ITA BA.SUN YI CIRKO CIRKO SAI KWATSAM AISHA TA SHIGO TASHAIDAWA HAJIYA GA ALHAJI YA ISO. NAN DA NAN MANGA YA TUREMUTUMIN NAN A WANI D’AKI YA KULLE.ALHAJI YA SHIGO GIDA YA ISKE HAJIYA DA MANGA SUN YICIRKO CIRKO A FALO. YA TAIMBAYE SU ME KE FARUWA? DOMINYA LURA GA JAKA AN CIKA DA KAYA AN YAR A K’ASA. HAJIYATA FAD’A MASA WAI MANGA NE KE SO YA YI TAFIYARSA GIDAYA GAJI BAI DA KUD’I. ALHAJI YA RARRASHE SHI. DA GANINALHAJI YA D’AN D’AUKE HANKALINSA DAGA KAN SU, SAIMANGAYA YI SAURI YA BUD’E WATA K’OFA YA TURA MUTUMIN NANZUWA K’OFAR FITA WAJE.ALHAJI YA JUYO DA HANKALINSADOMIN YA SO YA FAHIMCI ABIN DA YA GUDANA, AMMA AKASHASHANTAR DA SHI. MANGA YA D’AUKE JAKAR SA YA MAYAR .HAJIYA DA ALHAJI SUKA ZAUNA A FALO SUKA D’AN FARARAHA, BA DA DAD’EWA BA ALHAJI YA SHIGA CIKI ITA KUMATA TASHIDA NIYYAR HAD’A MASA ABIN DA ZAI SHA.SUNA ZAUNE FALO SU UKU, ALHAJI DA HAJIYA DA MANGA, SHIALHAJI YANA BA MANGA HAK’URI HAR MA YANA FAD’A MASACEWA YA YI MASA TSARABA TA SAMARI, KAYA IRIN NA NIGOGIKAMAR YADDA HAJIYA TA SO. MANGA YA YI MURNA. HAJIYADA MANGA SUKA FARA SUKAR MISBAHU WAJEN ALHAJI, TUNALHAJI YANA MAMAKIN YADDA MISBAHU ZAI CI AMANAR SAHAKA,HAR DAI YA HARZUK’A SOSAI. BAYAN SUN HARZUK’A SHI, SAIKUMA SUKA FICE YAWON SU DA NIYYAR MANGA ZAI KAI TAGIDAN WATA K’AWAR TA.AISHA TA SAMI MISBAHU A WAJE TA SANAR DA SHI CEWAALHAJI YANA SON GANINSA. MISBAHU YA TAMBAYE TA HALINDATA GA ALHAJI. AISHA TA SHAIDA MASA CEWA, HAKIKA ALHAJIYANA CIKE DA B’ACIN RAI. MISBAHU YA FAD’A WA AISHAFAHIMTAR DA YA YI HAJIYA TANA K’ULLA MASA SHARRI AWURIN MAIGIDANSA. AISHA TA FAD’A MASA ITA MA YADDAHAJIYAKE TA NEMAN SU DA SHARRI ITA DA ALIYU. AISHA TA FITATANA TUNANI. DAGA NAN SAI AKA SHIGA WATA WAK’ATSAKANINAISHA DA MISBAHU.HAJIYA TA FITA WAJE TA KIRA MANGA SUKA TATTAUNA AKANJUNA BIYU DA TA KE DA SHI, DA KUMA YADDA ZA SUSHIRYA MAKIRCI AISHA MA TA SAMI JUNA BIYU. SUKA SHIRYAZUWA INDA ZA SU ZUBAR DA CIKI. SUKA KUMA SHIRYA YADDAZA SU SA ALHAJI YA AMINCE WANI ABOKIN MANGA DA ITAHAJIYA TA NUNA WA ALHAJI YA FI DACEWA YA AURI AISHAZAID’AUKE TA ZUWA GAIDA MAHAIFIYAR SA. SHAWARA TAKAMMALA, HAJIYA TA KOMA CIKIN GIDA, MANGA KUWA SAI YAYIDARIYA IRIN TA K’ETA.ALHAJI YASA MISBAHU A GABA YANA TA BALBALE SHI DAMUSIBA. HAJIYA DA MANGA SUKA SHIGA FALON SUKA SAME SU.ALHAJI YA CE YANA SON MISBAHU YA YI MASA BAYANIN YADDAWASU KUD’I MASU YAWA SUKA SALWANTA. MISBAHU YA CEKANSA NA CIWO A BAR SHI HAR SAI YA SAMI SAUK’I. HAJIYADA MANGA SUKA K’ARA ZUGA ALHAJI DA WASU ZARGE ZARGENA DABAN AKAN MISBAHU. ZUCIYAR ALHAJI TA KAI K’ARSHEGA ZAFI HAR YA FARA DUKA DA HARBIN MISBAHU.MISBAHU YA NEME ALHAJI YA SAURARA MASA, AMMA INA!AISHA TA JE TA SAMI ALIYU SUKA RIK’A ZANTAWA A IRINHALIN DA MISBAHU KE CIKI. ALIYU YA SHA ALWASHIN IN DAIAN YIDUNIYA DAN MANZO, TO SAI YA TAIMAKI MISBAHU. A WANNANHALI AKA SAKAYA MISBAHU.HAJIYA TALATU TA SALLAMA A GIDAN HAJIYA ZUHRA. TASAMI MANGA TARE DA HAJIYA A FALO SUNA HIRA. DA GANINHAJIYA TALATU SAI MANGA YA TASHI DA MURNA YA TARBE TA,AMMA ITA SAI TA KAUCE MASA. MANGA YA FITA YA BAR SU,HAJIYA ZUHRA TA TUNATAR DA ITA CEWA MANGA NE FA.HAJIYA TALATU TA CE TA SANI SARAI HANYA CE DAI SUKARABA.HAJIYA TALATU TA BA K’AWAR SHAWARA CEWA ITA MA TA FITAHANYAR MANGA DA NAKONGO. HAJIYA TALATU TA SANARDA K’AWAR TA WANI ABU DA KE DAMUNTA, WATO B’ACEWARK’ANIN TA TUN YANA YARO. HAJIYA ZUHRA TA FAD’A MATACEWA, AI KUWA A GIDAN NAN NASU AKWAI WANI YARO DA AKATSINTA A HANYA. SUKA YI YARJEJENIYA ZA TA TURA MATAALIYU HAR GIDAN TA DOMIN TA GAN SHI.NAKONGO YA SHIRYA IRIN NASA MAKIRCIN YA D’AUKI WATAYARINYA YA JE GIDAN ALHAJI YA CE SHI KAWUN HAJIYA NE.YARINYAR DA SUKE TARE KUMA WAI Y’ARSA CE YA KAWO WAJENHAJIYA DOMIN TA D’AN KWANA BIYU A WURIN TA.ALHAJI KUWA YA KARB’E SU HANNU BIBBIYU, YA SHIGA YAKIRA HAJIYA. HAJIYA NA GANIN NAKONGO SAI RAN TA YAB’ACITA SAN AKWAI WANI K’ULLI.TA KAIKAICI IDON ALHAJI TAHARARI NAKONGO, SANNAN KUMA TA YAUDARI ALHAJI TA GAIDANA NAKONGO A MATSAYIN KAWUN TA. HAJIYA TA K’I AMINCEWADA YA BAR Y’AR SA A WURIN TA. ALHAJI KUWA YA CE SHIYA AMINCE A BAR TA KAWAI. NAKONGO YA KARB’I GUZURI DAALHAJI YA MIK’A MASA, YA KUMA YI GODIYA, YA KAMA HANYAYA YI TAFIYAR SA YA BAR Y’AR SA A GIDAN. NAKONGO YA YIHAKA NE, DOMIN DUK DA SHI YA KAI MANGA WURIN HAJIYA,AMMA SU BIYUN DUKA SUN MANTA DA SHI.ALIYU YA JE YA YI SALLAMA A GIDAN HAJIYA TALATU. BAYANDOGON TUNANI SAI HAJIYA TALATU TA GANE ALIYU DAISHI NE K’ANIN TA DA YA B’ACE. SUNA CIKIN SHIRYA YADDAZA SU TAFI GARIN SU TARE, SAI HAJIYA ZUHRA TA SHIGOTAREDA WANI D’AN DABA. D’AN DABA YASA WA ALIYU BINDIGA AWUYA, DOMIN ITA HAJIYA ZUHRA RAN TA BAI BA TA BA, TANAZARGIN SU DUKA. BA A KASHE SU BA, AMMA TA SA SU AKULLE.DA HAJIYA ZUHRA TA KOMA GIDA, SAI TA KIRA SALAMATU TAJA KUNNEN TA DANGANE DA LURA DA TA YI TANA SHISSHIGEWA MIJIN TA. SALAMATU KUWA ASHE TSAGERA CE, TA TACEHAJIYA TA JUYA TA SHIGA CIKIN GIDA, TA BAR HAJIYA DAJUYAYI.RANAR DAI ALLAH YA KUSA TONA ASIRIN NAKONGO, DOMIN YAZO GAIDA SU ALHAJI, SAI GA WANI ABOKIN ALHAJI WANDATSOHON ABOKIN SHASHANCIN SHI NAKONGO NE, WATO YA SANSHI SARAI. NAN DA NAN NAKONGO YA JUYA YA TAFI KOGAISAWA DA HAJIYA DA SALAMATU BAI TSAYA YA YI BA.HAJIYA NA TA SHA’ANIN GABAN TA ITA DA MANGA, SU FITALOKACIN DA SUKE SO, KUMA SU KOMA GIDA DUK LOKACIN DASUKA GA DAMA. RANNAN SAI MA SUKA CE WA ALHAJI ZA SU YITAFIYA ZUWA GIDA GAIDA IYAYEN SU, AMMA BA SU BUKA-TAR MOTAR SA. ALHAJI YA YI JIMAMIN SHIGA MOTAR HAYA,AMMA SU SUKA NACE CEWA SUN FI SON HAKA D’IN. ALHAJIYA SA MUSU IDO SUKA YI TAFIYAR SU.ALHAJI MIJIN HAJIYA BAI K’ETARE MAGANAR HAJIYA BA TAAIKA WA DA Y’AR SA ZUWA GAIDA MAHAIFIYAR SAURAYINDA HAJIYA TA ZAB’A MATA. SAURAYI YA D’AUKI AISHA SUKATAFI BA DON RAN TA YA SO BA. DA SUKA ISA BAMAHAIFIYARSABA ALAMAR TA, SAI YA FITA YA ZUBA MUSU LEMO YANA TARAWAR JIKI. A WAJEN HAD’A LEMON, SAI YA ZUBA MAGANI ACIKIN WANDA ZAI BA AISHA. YA DAWO YA AJIYE WA AISHAWANDA YA SO TA SHA, SHI KUMA YA AJIYE NASA A GEFENSA.AISHA TA DAMU DA YA KIRA MAHAIFIYARSA DOMIN TA GAISHETA SU TAFI. YA TASHI YA LEK’A WAJE A CIKIN YAUDARA.KAFIN YA DAWO SAI A’ISAHA A D’AUKI LEMO TA FARA SHA.YANA DAWOWA, SAI YA D’AUKI NASAKOFIN LEMO YA FARA SHA.ALLAH MAI IKO ASHE AN SAMI KUSKURE, YA SHA LEMON DA YAKAMATA A’ISHA CE ZA TA SHA. NAN TAKE YA YI LAUSHI YAYISHAME SHAME. GANIN HAKA SAI AISHA TA GUDU.DA HAJIYA TA KOMA GIDAN ALHAJI TARE DA MANGA, SAIALHAJI YA NUNA MUSU B’ACIN RAN SA, DOMIN SUN K’ARAKWANABIYU AKAN KWANA BIYUN DA YA BA SU, SUN YI KWANA HUD’UKENAN. HAJIYA TA CE MANGA NE YA YI RASHIN LAFIYA.ALHAJIYA KALLE SU KAWAI YA KAU DA KAI.RANAR NAN ALHAJI YA ISKE Y’AR SA A’ISHA ITA D’AYAZAUNE A FALO. YA TAMBAYE TA INDA HAJIYA TA JE, TA CEMASA SUNFITA DA MANGA, SALAMATU KUMA TANA D’AKI. ALHAJI YANEMI JIN TA BAKIN A’ISHA IDAN DA ZAI AURI SALAMATU. DAFARKOA’ISHA TA YI ZATON BA ZAI YIWU BA TUN DA AN CE K’ANWARHAJIYA CE, AMMA DAGA BAYA SAI TA AMINCE DA YA NUNAMATA ABIN BA YADDA TA KE ZATO BA NE.HAJIYA DAI ASIRIN SU YA GAMA TONUWA, DOMIN KUWA WANNANABOKI NA ALHAJI YA LABARTA WA ALHAJI KOMAI DAKOMAI GAME DA NAKONGO. HAKA KUMA MAHAIFIYAR HAJIYA TAZO GANIN SU A LOKACIN DA ITA HAJIYA DA MANGA SUKA YITAFIYAR NAN TA KWANA HUD’U DA NIYYAR ZUWA K’AUYEN SU.DALILIN ZUWAN MAHAIFIYAR, SAI ALHAJI YA FAHIMCICEWA ASHE HAJIYA BA TA HAD’A KOMAI DA MANGA BA, DOMINMAHAIFIYAR TA SHAIDA MASA CEWA BA SU DA WANI MANGA ADUK ZURI’AR SU. ITA HAJIYA ZUHRA MA BA TA DA WATA Y’AR‘UWA BALLE TA HAIFI WANI D’A MANGA.ALIYU DAI YA B’ACE A TUNANIN AISHA DA ALHAJI. HAJIYAZUHRA TA YI SA’AR SA A SACE SHI DA HAJIYA TALATU DOMINA HALAKA. TO AMMA DA YAKE MISBAHU YANA HANNUN Y’ANSANDA, SAI Y’AN SANDA SUKA CI GABA DA BINCIKA HARHAJIYADA MANGA. A CIKIN WANNAN K’OK’ARI NE SUKA SAMI ALIYUDA HAJIYA TALATU AN TAFI DA SU WANI DAJI ZA A KASHESU.BAYAN AN SHA ARANGAMA, SAI Y’AN SANDA SUKA KUB’UTAR DAALIYU DA HAJIYA TALATU.ALHAJI YA TONA WA HAJIYA DUKA ASIRRAN TA DA YA GAMATARAWA. Y’AN SANDAN DA SUKA ZO DA SU ALIYU DA H.TALATUKUMA, SAI SUKA TAFI DA HAJIYA ZUHRA DA MANGA.MISBAHU YA BAYYANA WA ALHAJI YADDA WATA RANA HAJIYA TASHIRYA MASA SHARRI TA SA YA MATSA KUSA DA ITA DONYA TAIMAKA MATA WAI WANI ABU YA SHIGA A RIGAR TA HARTANA TA KUWWA, AMMA YANA MATSAWA, SAI MANGA YA FITODA ABIN D’AUKAR HOTO YA D’AUKE SU. HAJIYA TA TSARE SHIKO YASA MATA HANNU A CEKIN NA KUD’I KO KUMA A NUNAWA ALHAJI HOTUN. WANNAN YASA ALHAJI YA GA BA MILIYANUKU A CIKIN KUD’INSA.ALHAJI YA YI NADAMA AKAN SAKACIN SA, SUKA YAFE WAJUNA, SHI ALHAJI YA AURI SALAMATU, SHI KUMA ALIYU ZAIAURIA’ISHA. AKA RUFE FIM D’IN DA WAK’AR SOYAYYA TSAKANINALIYU DA A’ISHA.FAM FAM FAM !!!KUSAKURAI :
I. BA A KIRAN UWA MAHAIFIYA DA YAKUMBO (KO ANA YI NE AKANO ?)
II. BAI YIWUWA NAMIJI NA AUREN MACE TSAWON SHEKARU BAISAN Y’AN ‘UWAN TA NA KUSA BA
III. BAI YIWUWA MACE TA ZAUNA DA WATA YARINYA A GIDANTA HAR TA SHIGE WA MIJINTA BA DA SON RANTA BA
IV. BAI YIWUWA YADDA KUSACIN HAJIYA TALATU YA KE DAHAJIYA ZUHRA A CE BA TA FAHIMCI LABARIN ALIYU BADAGA GARE TA TUN DA DAD’EWA. KUMA A LOKACIN DA TABA TA LABARIN SA DA BA ZA TA BAR GIDAN BA SAI TAGAN SHI, DOMIN AI TANA NEMAN SA RUWA A JALLO KUMAGA ALAMA SHI NE
V. HAJIYA ZUHRA TANA KUSA TANA SAURAREN DUK ABINDA KEGUDANA A TSAKANIN H.TALATU DA ALIYU, BAI KAMATATA YI ZATON WANI ABU DA BA WANNAN BA
VI. SAUTI YA YI YAWA TA YADDA YA KAN HANA A JI MAGANAWANI LOKACI
VII. ANYA AKAN IYA YIN SHEKARA ASHIRIN MALAMIN ALLOBAI MAYAR DA YARO YA GA IYAYENSA BA?ILMANTARWA:FIM D’IN YANA YIN NASIHA NE GA WASU IRIN MAZA MASUSAKACI MATUK’A. WANNAN ZAI SA KO WANE NAMIJI YA SHIGAROK’ON ALLAH YA KARE SHI DAGA SHARRNI WASU MATA. IDANDAI HAR MACE ZA TA IYA MAYAR DA NAMIJI HAKA, TO, MAZAKU TASHI TSAYE!INA ROK’ON AFWA AKAN NAWA KUSAKUREN, KAR A MANTAWANNAN SHI NE NA FARKO, KUMA NA YI SHI CI SAURI,DAN HAKA INA KUMA JIRAN JIN AMSOSHIN TAMBAYOYI NA.
NA GODE TAKU AMINA ABDULMALIK.

Tabbas wannan marubuciya tayi kokari sosai wajen tsefe fim din nan dalla-dalla,wanda idan mai karatu ma ya tsaya a nan to ba sai ma a kallai fim din ba,wannan sharhin ma ai ya isheshi.Dan haka malama Amina Allah ya kara basira.

Ga amsar wadannan tambayoyi naki dai dai gwargwado;
Martani/Amsoshin Sharhin Fin 'Aliyu'...



Na jidadi kwaraida gaske da ganin sharhin da kika yi akan film dina mai suna Aliyu.

Dan gane da kura-kurai da kika fitar kuwa shine kamar yada kika sani ne dika na mutum a duniya, idan zai yi wani abu to fa bazai rasa yin kuskure ba. Wasu daga cikin kurakuren munsanda su sai bayan mu gama aikin film din ne sannan muka farga kamar yadda masu iya Magana kan ce turan gini tinran zane. Zan so inyi dan sokaci akan wasu baga ci kin kurakuren nan guda shida da kika fitar, wannada ba iyawa kuma na yadda mun kamu.

Kince ba a kiran uwa mahaifiya da ya kumbo ko ana yin e a kano? Amsa: Bamu bata wani takamaiman suna ba ne cikin film din. Munyi anfani da sunnan da ta kan fito da shi a sauran filafilai da suka gabata.
Kince bai yuwa namuji na airen mace tsowan shekaru bai san yan uwan tan a kusa ba. Amsa: Wannan haka yake munyi kuskure a gafarce mu.
Kince bai yuwa mace ta zauna da wata yarinya a gidan ta, hart a shige wa mujinta bada so ranta ba. Amsa: Idan muka koma cikin shiren zamu ga cewa dole ne hajiya Zuhura ta yi hakurin zaman salamatu a gidan, domin kuwa da zarrar ta nuna wa Alh. Cewa ba kanwar ta bace to ita ma tata ta tashi da manga. Kuma Ai naKongo yakawo ta ne dan shi ma ya yagi rabon sa daga jikin Alh. Ganin ce wa baya samun komai daga su manga da Hajiya.
Kince baiyuwa yadda kusan cin Hajiya talatu yake da hajiya Zuhura a ce bata fahimci labirin Aliyu ba daga gare ta da dade wa kuma a lokacin da ta bada labarin sad a bazata bar gidan ba sai ta gansi domin ai tana neman sa ruwa a jallo kuma ga alama shi ne. Amsa: Hajiya Talatu kan dauki lokaci bata zo gidan hajiya Zurura ba. A salima de can wajen yawon su suke haduwa don haka kosun hadu da aliyu ba lailai net a gane shi ba. Saboda tin yana a shekara shida rabon sad a gida. Alokacin da a ke zance Aliyun ma shi y agama yan aikacen aikacen sa daya saba yi na gida yayi ficewar sa. Bayan da hajiya zuhura ta karfafa zancen Aliyu ne abin yazama jirwaye mai kamar wanka, tana ganinsa ainan take ta sheda shi.
kince hajiya Zuhura tana kusa tana sauraren duk abin da kike gudana sakanin hajiya Talatu da Aliyu bai kamata ta yi zatan wani abin ba wannan ba. Amsa: Ayi hajiya Zuhura ta finhim ce cewa tunda hajiya talatu ta nemi ta tura mata Aliyu kuma zance ya zo da haka, takuma san lalai wanni abu ka iya biyo baya ko muna finci ko tonan silili, sai kawai ta biyo baya.
Kince sauti yayi yawa ta yadda yakan hana a jimagana wani lokocin. Amsa: Mun kwana da sanni wanan masala a tare da mu tin bayen kamala aikin harhada hotuna na shirin. Yakasance dani (Aliyu) d director na da editor na wato Ahmed L Deneji zamu zauna a gaban computer tindaga karfe tara na dare har waye wa gari, munna aikin har tsahon kusa kwana bakwai. Ni bana barci da gudun kada a yi mun shirme amma sabo da sauri da kuma yawan barci iren na director nay a sa aka samu baraka ta wajen mai aikin tayadda ya sami yin gaban kansa. Kuma ni inna basi umarni sai ya ce min ba aiki na bane, wai ni dan wasa ne( Artist) dan haka munyi kuskure a nan, sai a gafarce mu.
Kince anya akan iya yin shekara ashirin malamin Alo ba mayar da yaro ya ga iyayen sa ba? Amsa: Eh! Namma fa kin yi gaskiya yakamata ko bayan shekara a ce ya koma gida ya yi noma, in ya so da kaka ya dawo cirani mun yi kuskure a gafarce mu.
To ina ganin a binda zan dan iyayin tsokaci/raddi/ko kuma ince amsoshin tambayoyin da kuma shawarwarin da kika yicikin shirin fim dinmu mai suna ‘Aliyu’ da fatan kin gamsu. Kuma tun ranar da naga sharhin kina karanta, nan na tabbatar cewa lallai kin fahimci inda fim din ya sa gaba, don kinfi yawancin mutanen da suka bamu shawarwari da kuma sharhi ta ‘internet’ ko ta akwatin gidan waya ko ta wayar tarho ko kuma gaba da gaba.Na gode
Naku Nura Na'iya Gwammaja
{Boudah Aliyu}